Isa ga babban shafi
Kwallon Kafa

Super Eagle na Najeriya sun doke Namibia

‘Yan wasan Super Eagle na Najeriya sun samu nasarar doke ‘Yan wasan Brave Warriors na Namibia da ci daya mai ban haushi a birnin Calabar. Ike Uche da ke taka kwallo a Spain ne ya zira wa Najeriya kwallonta a ragar Namibia.

'Yan wasan Super Eagle na Najeriya a lokacin da suke fafatawa da 'Yan Peru
'Yan wasan Super Eagle na Najeriya a lokacin da suke fafatawa da 'Yan Peru REUTERS/Pilar Olivares
Talla

Yawancin ‘Yan wasan da suka taka kwallo matasa ne kodayake akwai John Utaka na Montpellier ta Faransa cikin tawagar ta Super Eagle.

Namibia sai ta sake kara kwazo domin a ranar Assabar zata kara da Kenya Bayan ta sha kashi a Najeriya.

A ranar Assabar, 'Yan wasan Sudan sun lallasa Zambia mai rike da kofin Afrika ci 2-0.

Kasar Jamhuriyyar Benin kuma ta doke Mali ci 1-0.

Wasa tsakanin Uganda da Angola, sun yi kunnen doki ne ci 1-1. Togo da Libya suka yi kunnen doki 1-1.

Wasa tsakanin Jamhuriyyar Nijar da Gabon, an tashi ne babu ci a birnin Yamai.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.