Isa ga babban shafi
Kwallon Kafa

Kamaru da Senegal sun samu nasara a wasannin sada zumunci

Kasar Kamaru da Senegal sun samu nasarar lashe wasannin sada zumunci da aka gudanar a karshen mako kafin fara buga wasannin neman shiga gasar cin kofin Duniya a watan Yuni.

Samuel Eto'o tare da Alexandre Song 'Yan wasan Kamaru. hukumar kwallon kafar Kamaru ta haramtawa Eto'o buga wasanni
Samuel Eto'o tare da Alexandre Song 'Yan wasan Kamaru. hukumar kwallon kafar Kamaru ta haramtawa Eto'o buga wasanni Clive Mason/Getty Images
Talla

Senegal ta doke Morocco ne ci 1-0, Mousa Konate ne ya zirawa Senegal kwallonta a ragar Morocco.

A faransa kuma Kasar Kamaru ta lallasa Guinea ci 2-1.

Jamhuriyyar Nijar kuma tasha kashi ne hannun Algeria ci 3-0, kamar yadda Saliyo tasha kashi hannun Jordan.

Amma wasa tsakanin Burkina Faso da jamhuriyyar Benin an tashi ne ci 2-2.

Wasa tsakanin Mozambique da Nimibia a kasar Jamus an tashi ne babu ci 0-0.

Haka ma wasa tsakanin Tanzania da Malawi a Dar es Salam an tashi ne babu ci 0-0.

A ranar 1 ga watan Yuni ne kasashen Afrika zasu buga wasannin neman shiga gasar cin kofin Duniya da za’a gudanar a shekarar 2014. A tsakiyar watan ne kuma kasashen zasu buga wasannin neman shiga gasar cin kofin Afrika da za’a gudanar a badi.

Kasar Kamaru dai zata kwashe makwanni uku a jere tana buga wasa inda zata kara da Jamhuriyyar Demokradiyar Congo da Libya a wasannin neman shiga gasar cin kofin Duniya sai kuma wasa tsakanin Kamaru da Guinea Bissau a wasannin neman shiga gasar cin kofin Afrika.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.