Isa ga babban shafi

Jagoran 'yan adawar Venezuela na zargin gwamnati da kitsa hari a kan sa

A Venezuela, jagoran yan adawa Juan Guaido  ya zargin wata kungiya dake da halaka da gwamnatin Nicolas Maduro da kai masa hari a lokacin da ya kaddamar da rangadi  cikin kasar ta Venezuela.

Jagoran yan adawar kasar Venezuela  Juan Guaido
Jagoran yan adawar kasar Venezuela Juan Guaido AP - Matias Delacroix
Talla

Dan adawar a wani faye-fan bidiyo da aka yada ,ya na mai nuna ta yada aka shiya masa kwantar bauna a wani lokaci da ya shirya ganawa a wani gidan  cin abinci da wasu magoya bayan jam’iyya mai adawa a birnin San Carlos dake yankin Cojedes a tsakiyar kasar.

Jagoran yan adawa na kasar ta Venezuela na zargin gwamnati da kitsa wannan aika-aika.

Juan Gaido da ya samu tattaunawa ta wayar talho da Shugaban Amurka  Joe Biden ranar laraba da ta gabata,na ci gaba da samun goyan bayan kasar ta Amurka,wacce ta ki gayyatar Shugaban kasar Nicolas Maduro a taron kasashen yankin Amurika.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.