Yemen-Saudiya
An Bude Taro a Saudiyyar don Warware rekicin Yemen, 'Yan Houthi sun ki halarta
An bude taron kasashen larabawa yau lahadi a birnin Riyadh na Saudiyya da niyyar duba a’lamarin yakin kasar Yemen.Sai dai kuma bangaren Houthi, ‘yan tawayen Yemen dake neman kawar da Gwamnatin su sunki halartan wannan taro.Taron na zuwa ne yau lahadi, rana ta karshe cikin kwanaki biyar na tsagaita wuta domin kai kayan agaji ga mabukata dake Yemen.Shugaban Yemen Abd-Rabbu Mansour Hadi dake gudun hijira zai yi jawabi a taron na yau.Bayanai na nuna duk da tsagaita wuta da akayi anyi ta samun hare-hare a wasu sassan kasar ta Yemen.
Wallafawa ranar: