Isa ga babban shafi
Faransa-Falasdinawa

Faransa zata amince da ‘Yancin Falasdinawa

‘Yan Majalisun kasar Faransa daga bangaren Jam’iyar gurguzu na shirin gabatar da wani kudiri da zai bukaci gwamnatin kasar ta amince da kasar Falasdinu makwanni bayan Majalisar kasar Birtaniya ta amince da haka. Bukatar ta biyo bayan rushewar tattaunawar zaman lafiyar da ake tsakanin Isra'ila da Falasdinawa da kuma yakin da aka yi a Gaza wanda ya kai ga kashe Falasdinawa sama da 2,000.

Shugaban Faransa, François Hollande
Shugaban Faransa, François Hollande REUTERS/Alain Jocard
Talla

Majalisar Faransa ta bukaci gwamnatin kasar ta yi amfani da makamin amincewa da kasar Falasdinun wajen tilastawa Isra’ila kawo karshen gine ginen da ta ke yi a Yankunan Falasdinawa.

Kasar Sweden ce kasa ta farko a Turai da ta sanar da amincewa da kasar ta Falasdinu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.