Faransa da Jamus za su aika da rundunar Soji a Mali
Faransa da Jamus sun amince su aika da rundunar Soji ta hadin gwiwa a tsakaninsu zuwa ƙasar Mali domin aikin horar da sojojin ƙasar bayan sun yi wata ganawar tsaro a birnin Paris. Babu cikakknen bayani akan adadin Sojojin da ƙasashen biyu zasu aika a Mali amma wannan mataki ne da ƙasashen suka ɗauka domin taimakawa Jami’an tsaro a Afrika.
Wallafawa ranar:
Faransa da Jamus sun kafa rundunar Soji ne tun a 1989 a lokacin yaƙin duniya na biyu.
Dakarun Faransa ne dai suka taimakwa ƙasar Mali dawo da Mulkin Dimokuradiya bayan ƙasar ta abka cikin rikici a 2012 a lokacin da ƴan tawaye suka karɓe ikon yankin arewaci bayan Sojoji sun hamɓarar da gwamnatin Amadou Toumani Toure.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu