Kasar Amurka ta fara kwashe ma’aikatan ofishin jakadancinta dake Siriya.
A yayin da kasar Amurka ke ci gaba da yunkurin kai hari akan kasar Syria, a yanzu haka Amurkan ta fara kwashe kananan ma’aikatanta dake ofishin jakadancinta a Beirut, sanna ta umarci Amurkawa da su guji yin tafiya zuwa yankin Lebanon da kudancin Turkiya, wato kasashen dake makwabtaka da kasar ta Siriya.
Wallafawa ranar:
Wannan umurni da hukumommin Amurkan suka bayar na zuwa ne a daidai lokacin da Shugaban Barack Obama ke ci gaba da neman goyon bayan kasashen duniya akan kai hari a Siriya.
Shugaba Obama yace, ba zai yuwu su cigaba da rufe idanu ga zahirin abunda suka gani ba a kasar siriya.
Abinda yasa yayi kira ga yan majalisun kasar daga dukkan jam’iyyun biyu na kasar ta Amurka, dan su tunkari manufar da suke da ita ga kasashen duniya da kuma
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu