Isa ga babban shafi

Faye ya nada Ousmane Sonko a matsayin Firaministan Senegal

Sabon shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye ya nada Ousmane Sonko mukamin Firaminista a kasar ta yammacin Afrika, wanda ke matsayin tsohon ubangidansa kuma tsohon dan takarar shugabancin kasa da ya yi takun-saka da tsohon shugaba Macky Sall.

Ousmane Sonko tare da Bassirou Diomaye Faye.
Ousmane Sonko tare da Bassirou Diomaye Faye. AFP - JOHN WESSELS
Talla

Jim kadan bayan kammala shan rantsuwar fara aiki ne shugaba Faye ya sanar da nadin Sonko a matsayin Firaminista kuma tuni tsohon babban abokin gabar na Macky Sall ya amsa mukamin tare da bayyana shirinsa na mika sunayen ministocin da ya ke shirin kafa majalisa da su.

Babu dalilin da zai hana ni karbar mukamin Firaminista

A jawabinsa na karbar mukamin na Firaminista, Sonko ya ce bai ga dalilin da zai hana shi karbar mukamin ba, maimakon haka yanzu ne lokacin da ya kamata ya mara baya ga Faye don ganin ya samu nasara a mulkinsa musamman wajen cika alkawurran da ya daukar wa al’ummar Senegal.

Ousmane Sonko, na jawabi ta kafar talabijin
Ousmane Sonko, na jawabi ta kafar talabijin © RFI MANDENKAN
A gaban dubban daruruwan al’ummar Senegal da kuma wakilcin shugabannin kasashen Afrika da dama ne Faye mai shekaru 44 ya yi rantsuwar kama aiki a jiya Talata.

Sabon shugaban kasar na Senegal da ke matsayin mafi karancin shekaru a tsakanin takwarorinsa na nahiyar Afrika, bai taba rike wani mukamin gwamnati ba gabanin nasarar ta lashe zaben shugaban kasa kwanaki 10 bayan fitar shi daga Yari.

Tsawon shekaru 2 Sonko mai shekaru 49 ya shafe yana fada da gwamnatin Senegal wanda ya kai ga mabanbantan zanga-zanga da kame da ma kisan tarin fararen hula yayin arangamar da suka rika da jami’an tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.