Isa ga babban shafi
JUYIN MULKI

Kungiyar Francophonie ta kori Nijer daga cikinta.

Komitin dindindin na kungiyar Francophonie (CPF) ya dakatar da jamhuriyar Nijer daga cikin kungiyar, tare da bukatar ganin sakataren kungiyar,  ya ci gaba da tuntubar mahukumtan na Nijer,  da zummar tsayar da ruwan miya kan batun komawar kasar kan tafarkin demokradiya, kamar yadda kungiyar ta OIF bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya juma’a.

Alamar tutar kungiyar Francophonie, ta  kasashen da suke amfani da harshen Faransanci.
Alamar tutar kungiyar Francophonie, ta kasashen da suke amfani da harshen Faransanci. © Wikipedia
Talla

A dai gefen kuma kungiyar Ecowas ko Cedeao  a makon da  ya gabata,   ta yi  wata ganawa da  mahukumtan jamhuriyar Nijer, karkashin jagorancin shugaban kasar Togo  ta bayyana cewa, bangarorin biyu sun cimma matsaya kan batutuwan da zasu tattauna a kai, da suka hada da  wa’adin da sojoin za su dauka a karkashin gwamnatin ta rikon kwarya kasar  

Tattaunawar bangarorin biyu dai ta ta’allaka ne kan battun wa’adin mulkin rikon kwaryar, bayan da tun farkon da farko bayan juyin mulkin sojoji suka bayyana,  kebewa kansu wa’adin shekaru 3 kafin su mika Mulki ga hannun wata gwamnatin farar hula

Sai dai ita kuma kungiyar ta CEDEAO ta kafe ne, a tsakanin watanni 15 zuwa 18 na wa’adin  rikon kwaryar

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.