Isa ga babban shafi

Zazzabin Dengue ya kashe sama da mutane 214 a Burkina Faso cikin wata 10

Mahuknata a Burkina Faso sun  ce wata cuta da sauro ke yadawa da ake kira zazzabin Dengue ya lakume rayuka dari 2 da 14  tun daga ranar 1 ga watan Janairun wannan shekara, akasari a birnin Ouagadougou da Bobo-Dioulasso, birin na biyu mafi girma a kasar. 

Saura da ake zargin ke haddasa zazzabin Dengue
Saura da ake zargin ke haddasa zazzabin Dengue Rafael Neddermeyer
Talla

Cikin wata sanarwa ma’aikatar lafiyar kasar da ke yammacin nahiyar Afrika ta ce daga ranar 1 ga watan Janairun wannan shekarar zuwa 15 ga watan Oktoba an samu mutane dubu 50 da dari 4  da 78 da suka harbu da wannan cuta, inda daga cikin su mutane 214 suka mutu. 

Yaduwar cutar cikin sauri

Sanarwar ta ce daga ranar 9 zuwa 15 ga watan Janairu shekarar 2023 kawai sama da mutane dubu 10 ne suka kamu da wannan cuta, aka samu mace-mace 48, kuma biranen Ouagadougou da Bobo-Dioulasso ne wannan cuta ta fi kamari, a cewar ministan lafiya, Robert Lucien Jean-Claude Kargougou.  

kamanceceniya da zazzabin Malaria

Zazzabin Dengue, wanda sauro ne ke yadawa, yana da alamomi masu kamanceceniya da zazzabin Malaria, wanda ke yaduwa a kasashen da ake da yanayi na zafi, inda yake kama mutane miliyan 100 zuwa 400 a duk shekara, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya. 

A shekarar 1960 ce wannan cuta mai sanya zazzabi mai zafi, ciwon kai, jiri da amai, wani lokacin ma zubar jini ta fara bulla a Burkina Faso, amma a shekarar 2017 ce aka mayar da hankali a kanta, bayan ta kashe mutane 17. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.