Isa ga babban shafi
Burundi

Tarayyar Turai ta gargadi Burundi

Ministocin Kungiyar kasashen Turai sun ce a shirye suke su sake kakabawa kasar Burundi Karin takunkumin kariyar tattalin arziki sakamakon kasa kulla yarjejeniyar kawo karshen tashin hankalin da ake samu a kasar wanda yanzu haka ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 440.

Ana ci gaba da kai hare hare a Burundi
Ana ci gaba da kai hare hare a Burundi STRINGER / AFP
Talla

Tarayyar Turai ta bayyana damuwa kan rashin mutunta yarjejeniyar Cotonou.

Akwai dai Hukumar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International da tace ta gano wasu manyan kaburbura guda biyar a kusa da Bujumbura inda jami’an tsaron Burundi suka binne gawarwakin mutanen da suka kashe.

Burundi ta fada cikin rikici tun a watan Afrilun 2015 lokacin da shugaban kasar Pierre Nkurunziza ya ayyana matakin neman wa’adin shugabanci na uku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.