Yunkurin tube shugaban PDP daga mukaminsa a Najeriya
Wasu ‘ya‘yan jam’iyyar PDP a Nigeria sun shigar da kara a gaban wata babbar kotun kasar, inda suke neman a dakatar da yunkurin da suka ce ana yi, na tursasa wa shugaban jam’iyyar Adamu mu’azu domin ya yi murabus.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wasu majiyoyi a kusa na jam’iyyar sun rawaito cewa Tasiu Iliyasu Hussaini da Waziri Amadu, suna neman kotun ta dakatar da uwar jam’iyyar daga rushe kwamitin gudanarwar jam’iyyar, ko tilastawa membobin kwamitin su ajiye aikinsu.
Jam’iyyar ta PDP wadda ta share tsawon shekaru 16 akan karagar mulkin Nigeria, ta shiga rudani ne jim kadan bayan kammala babban zaben kasar wadda ta sha kaye a hannun jam’iyyar adawa ta APC.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu