Tunisia
Ana Cigiyar 'Dan Bindiga Daya a Harin Tunisia
Jami'an tsaro a kasar Tunisia sun tsaurara matakan farautan wani mutun daya daga cikin ‘yan bindiga uku da suka kai kazamin hari wani gidan ajiyan kayan tarihi a birnin Tunis inda suka kashe mutane 21.Shugaban kasar Beji Caid Essebsi ya fadi cewa ‘yan bindiga uku ne suka kai harin kuma mutun daya ya samu ya tsere, amma mutun biyu an kashe su nan take.Hukumomin kasar dai sun gabatar da wani hoton bidiyo da ta dauko hotunan ‘yan bindigan a lokacin da suke aiwatar da barnan.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: