“Amurka ba zata turo da dakaru a Afrika ba”
Kasar Amurka tace bata da wata niyyar girke sojojin ta a Nahiyar Afrika don magance tashe-tashen hankulan da suka addabi wasu kasashen Yankin, sai dai tace zata taimakawa sojojin kasashen samar da zaman lafiya da horo. Mai bai wa shugaba Obama shawara kan harkokin tsaro Susan Rice ta bayyana haka kwanaki kafin kusan daukacin shugabanin Nahiyar su ziyarci kasar don ganawa da shugaba Barack Obama.
Wallafawa ranar:
Rice tace Amurka ba ta tunanin jibge sojojinta a Afrika, sai dai zata taimakawa Nahiyar wajen magance ta’addanci musamman matsalar Boko Haram da Mayakan Al Shebaab da Al Qaeda.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu