Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Kiir da Machar zasu hau teburin sulhu

Ma’aikatar harakokin wajen Sudan ta Kudu tace Shugaban kasar Salva kiir ya kama hanya zuwa Addis Ababa domin halartar zaman teburin sulhu tare da Tsohon Mataimakinsa kuma kwamandan ‘Yan tawaye Riek Machar da suke rikici da juna tun a watan Disemban bara.

Riek Machar da Salva Kiir da ke fada da juna a kasar Sudan ta Kudu
Riek Machar da Salva Kiir da ke fada da juna a kasar Sudan ta Kudu REUTERS/Andreea Campeanu
Talla

Kasashen duniya suna fatar samu jituwa a tattaunawar tsakanin Machar da Kiir domin kawo karshe rikicin kasar da janyo hasarar rayuka da dama.

Tun a daren Alhamis ne, rahotanni suka ce Riek Machar ya isa birnin Addis Ababa inda za’a yi zaman tattaunawar ta keke da keke tsakanin shi da shugaba Salva Kiir da kuma mai shiga tsakani shugaban kasar Habasha.

02:35

Dr Laraba Abdullahi

Ramatu Garba Baba

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.