Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Chadi za ta janye dakarunta daga Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Taron shugabannin kasashen Afirka da na Tarayyar Turai da ke gudana a birnin Brussels, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga kokarin da kasashen duniya ke yi domin dawo da zaman lafiya a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

Sojojin Chadi a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
Sojojin Chadi a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya REUTERS/Siegfried Modola
Talla

To sai dai kamar yadda aka ji a labaran duniya, yanzu haka kasar Chadi, wato daya daga cikin kasashen da ke taimakawa domin shawo kan wannan rikici ta ce za ta janye dakarunta daga kasar.

Kasar Chadi dai ta bayyana daukar wannan mataki ne domin nuna bacin ranta dangane da abin da ta kira shi da suna cin zarafi da kuma bita da kulli da ake yi wa kasar, duk kuwa da kokarin da take na samar da zaman lafiya a can karkashin inuwar MDD.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.