Mali
Dakarun Faransa sun kashe mayakan sa-kai a Mali
Ministan tsaron Faransa Jean-Yves Le Drian, yace sojojin kasar da ke aiki a Mali sun kashe mayakan kungiyar Aqmi da dama a cikin kwanaki biyu da suka gabata a wasu hare-hare ta sama da suka kai akan maboyar mayakan da ke yankin Arewa maso gabashin Mali.
Wallafawa ranar:
Talla
Ministan tsaron yace farmakin ya biyo bayan tattara wasu bayanan sirri ne akan yadda magoya bayan kungiyar mai alaka da Al Qaeda da ke tafiyar da ayyukansu a yankin Ametetai da ke cikin tsaunukan kuma da ke kusa da iyakar Mali da Algeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu