Isa ga babban shafi
Najeriya

Amurka ta saka sunan Shekau cikin jerin sunayen ‘Yan Ta’adda

Gwamnatin Amurka ta saka sunayen shugabannin Kungiyar Boko Haram a Najeriya cikin jerin sunayen ‘Yan Ta’adda tare da bayyana kungiyar ta kashe mutane sama da 1,000 a jerin haren haren da kungiyar ta yi ikirarin daukar nauyi.

Abubakar Shekau, Shugaban Kungiyar Jama'atul Ahlis Sunnah Lidda'awati Wal Jihad, tare da wani Mambobin shi
Abubakar Shekau, Shugaban Kungiyar Jama'atul Ahlis Sunnah Lidda'awati Wal Jihad, tare da wani Mambobin shi AFP PHOTO / YOUTUBE
Talla

Mutane uku da aka saka sunansu sun hada da Abubakar Shekau da Abubakar Adam Kambar da Khalid Barnawi amma ba tare da saka suna kungiyar Boko Haram a jerin kungiyoyin ‘Yan Ta’adda ba na Duniya.

Gwamnatin Amurka ta ce Abubakar Shekau ne ta dauka matsayin shugaban Kungiyar Boko Hara amma Abubakar Adam Kambar da Khalid al-Barnawi suna da alaka ne da kungiyar Al Qaeda a reshen Maghreb.

Sanarwar daga Amurka tace Kungiyar Boko Haram ta dauki alhakin kai jerin hare hare da dama a Arewacin Najeirya karkashin jagorancin Abubakar Shekau.

A daya bangaren kuma rahotanni daga Najeriya sun ce Jami’an tsaro sun cafke Habibu Bama a Damaturu wanda ake zargin ya jagoranci kai harin ranar Kirsimeti da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 44.

Kafar Telebijin ta NTA a Najeriya ta tuwaito cewa an cafke Hsbibu Bama ne a garin Damaturu bayan musayar wuta da Jami’an tsaro

An dade Jami’an tsaro suna farautar Habibu Bama wanda ake zargin yana da hannun da harin da aka kai a ranar Kirsimeti a wata Coci a Madalla kusa da Abuja.

Gwamnatin Jahar Kaduna tace ta sassauta dokar hana fita ta sa’o’I 24 bayan barkewar rikici a Jihar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.