A kasar Senegal daruruwan mutane ne suka yi gangami a babban filin wasan kwallon kafa a Dakar, domin karrama fitaccen dan wasan kwallon kafar kasar Francois Bocande wanda ya mutu a ranar 7 ga watan Mayu a kasar Faransa.
Wata Kungiyar fararen hula a Jamhuriyar Nijar, ta bukaci kamfanin Areva, mallakar kasar Faransa, da ke hako ma’adinin uranium a kasar, biyan kudaden Diyya ga ‘Yan Nijar dai dai da yadda Kamfanin ke biyan Faransawan da suka mutu.
Gwamnatin Najeriya tace zata girke dakarunta a kasar Guinea Bissau don taimakawa kasar komawa ga mulkin fararen hula, kamar yadda kungiyar ECOWAS ta bukata.
A Yau Litinin ne Manyan Hafsoshin sojin kasashen Afrika ta Yamma zasu gudanar da wani taro a Abuja babban birnin Najeriya, don nazarin hanyoyin da zasu bi wajen girke dakaru a kasar Guinea Bissau da Mali.
Manyan Jami’an tsaron kasashen da ke raya tafkin Chadi, sun gudanar da taro a Jamhuriyar Nijar, don nazarin hanyoyin da zasu dakile safarar makamai da kuma ayyukan ta’adanci domin samun ci gaban kasashensu.
A kasar Libya mutane da dama sun samu rauni tare da samun mutuwar mutum daya sakamakon musayar wuta da aka yi tsakanin Jami’an tsaro da ‘Yan bindiga dwadanda suka yi zanga zanga a Hedikwatar Gwamnati a Birnin Tripoli.
A wani sabon Rahoto game da halin rayuwar iyaye mata da hukumar kare lafiyar kananan yara ta fitar, ya nuna Nijar ce kasar da iyaye Mata ke shan wahala bayan maye gurbin kasar Afghanistan a karon farko. Kasar Norway ce a matsayin kasa ta farko da iyaye Mata ke shan dadi a jerin kasashe 165 da aka kwatanta rayuwarsu.
Gwamnatin Jahar Flato a Najeriya ta sanar da haramta yin Acaba da babura a birnin Jos da kewaye, saboda yunkurin dakile ayyukan laifi da ake da baburan, kamar yadda ta sanar bayan taron Majalisar ...
A Yau Alhamis ne Shugabanin kungiyar kasashen Afrika ta Yamma, ECOWAS, zasu gudanar da wani taro na musamman don tattauna halin da ake ciki a kasashen Gunea Bisau da Mali.
Kungiyar Jama'atu Ahlus Sunnah Lidda'awati wal Jihad da aka fi sani da sunan Boko Haram a Najeriya, ta fitar da Wani hoton Bidiyo mai dauke da bayanin harin Ofishin Jaridar This Day tare da yin barazanar ci gaba da kai wasu hare hare a manyan kafafen yada labarai da ma'aikatansu a kasar.
Gwamnatin kasar Chadi ta yi kiran kasashen 16 a kungiyar raya tafkin Chadi domin samar da dakarun hadin kai don yaki da ‘Yan kungiyar Boko Haram da ke barazana ga sha'anin tsaro a Najeriya da makwabtanta.
Kungiyoyin kwadago a kasashen Turai sun shirya gudanar da zanga-zangar adawa da matakan tsuke bakin aljuhun gwamnati domin gudanar da hutunsu na ma’aikata. Ma’aikata a Spain sun shiga zangar zangar ne saboda matsalar rashin aikin yi.
Gwamnatin Sudan ta bada wa’adin mako daya ga ‘Yan kudancin Sudan 12,000 domin ficewa daga kasar Tare da kafa dokar hana fita akan iyakokin kasashen Biyu. A yau Litinin ne Majalisar Sudan zata yi muhawara akan kudirin dokar katse hulda da Sudan ta Kudu.
Mataimakin shugaban kasar Najeriya Namadi Sambo, ya yi kiran Kungiyar Boko Haram ta fito domin amincewa da tattaunawa don samun zaman lafiya a Najeriya, bayan wasu ‘Yan bindiga sun bindige mutane 20 a wajen Ibadar al’ummar Kirista a Jami’ar Bayero a Kano. Amma bayan kai harin Shugaban Kiristocin Jahar Kano Mista Ransom Bello, yace sun la’anci harin amma ba zasu mayar da martani ba.
An samu tashin bom a ginin Kamfanin Jaridar This Day a birnin Abuja bayan wani Bom ya tashi a Kaduna kusa da Ofishin Jaridar a kan titin Kontagora. Jami’an tsaro sun ce an cafke wani mutum da ake zargin ya dala Bom a Kaduna.
Kwamitin Lawan Faruk mai binciken badakalar bangaren Man fetir a Najeriya yace an sace kudade Dalar Amurka Biliyan Shida daga kudaden Tallafin Gwamnati a shekarun da suka gabata. Majalisar Wakilan Najeriya ta nuna bacin ranta kan yadda wasu jami’an Gwamnati da kamfanoni suke rub da ciki da dukiyar kasa da sunan tallafin man fetur.
Kwamandan dakarun Sudan yace sama da dakarun Sudan ta Kudu 1,000 ne suka mutu a lokacin yakin da sudan ta kaddamar a yankin Heglig mai arzikin Mai. Kamal Marouf yace Dakarun SPLM 1,200 dakarun Sudan suka kashe kafin su fice daga yankin a ranar Lahadi.