Akwai alamar Bincikar Qatar akan gasar cin Kofin duniya
Akwai yiwar Mahukuntan kasashen turai su bukaci hukumar kwallon kafa ta duniya ta sake gudanar da zaben bada damar daukan gasar cin kofin duniya ta 2022 da aka baiwa Kasar Qatar.
Wallafawa ranar:
A baya dai an ta samun cece-kuce akan yadda aka baiwa kasar ta Qatar izinin daukan bakwancin gasar cin kofin duniya.
Mahukuntan kasashen turai za su gudanar da taro a gobe alhamis, domin tattauna wannan batun
lamari da ke zuwa bayan samun wasu bayanai da ke cewar tsohon jami’in hukumar FIFA a kasar Qatar, Muhammad bin Hamman ya bada cin hancin kudi har dala miliyan 5 domin baiwa Qatar daman daukar nauyin gasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu