FIFA ta haramta wasan Najeriya da Ghana
Kasar Ghana ta fara neman kasar da za ta buga wasan sada zumunci da ita bayan hukumar FIFA ta soke wasansu da Najeriya da aka shirya gudanarwa a ranar 29 ga watan Maris a London. A ranar 26 Najeriya za ta buga wasan sada zumunci da Bolivia a Uyo akan haka ne FIFA ta soke wasan Najeriya da Ghana saboda kwanaki uku ne tsakani.
Wallafawa ranar:
A tsarin FIFA babu yadda kasa zata buga wasa a gida ta kuma tsallaka wata Nahiya cikin kwanaki uku.
Akan haka hukumar kwallon Ghana ta fara tuntunbar neman kasar da za ta buga wasan sada zumunci da ita a ranar da za ta fafata da Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu