‘Yan wasa suna kauracewa Ukraine
Wasu ‘Yan wasan kwallon kafa guda uku sun kauracewa kungiyar Volyn Lutsk ta Ukraine cikinsu har da Dan Najeriya, saboda kazamin rikicin da ake yi a gabacin kasar. ‘Yan wasan sun hada da Dan kasar Romania Eric Bicfalvi da Ramon Lopes na Brazil da Michel Babatunde na Najeriya, kamar yadda rahotanni suka tabbatar.
Wallafawa ranar:
A makon jiya kusan ‘Yan wasa guda bakwai ne suka kauracewa kungiyar Shakhtar Donetsk bayan harbo jirgin Malaysia a gabacin Ukraine.
Yanzu haka rahotanni sun ce ‘Yan wasa da dama ne na kasashen waje da ke buga kwallo a Ukraine ke son ficewa daga kasar saboda rikici.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu