Isa ga babban shafi
Girka

Ministocin Turai sun aminta a karawa Girka wa’adi

Ministocin Kungiyar kasashen Turai masu amfani da kurin yuro sun yi na’am da sabbin sauye sauyen da kasar Girka ta gabatar domin neman karin wa’adin watanni hudu kan bahsin da ake bin kasar. Sai dai Hukumar bayar da lamuni ta duniya da Babban Bankin kasashen Turai na dari-dari da sabon tsarin na Girka.

Firaministan kasar Girka Alexis Tsipras mai adawa da matakan Tsuke bakin aljihun gwamnati
Firaministan kasar Girka Alexis Tsipras mai adawa da matakan Tsuke bakin aljihun gwamnati Reuters/Marko Djurica
Talla

Girka ta gabatar da sabbin tsare tsaren ne a ranar Litinin kuma Ministocin kasashen na Turai 19 sun amince da sabon tsarin bayan sun tattauna ta wayar Tarho.

Amma dole sai Majalisar kasashen na Turai ciki har da Jamus da ke matsin lamba ga Girka sun amince da sabbin sauye sauyen kafin wa’adin da aka dibar wa kasar tun da farko ya kawo karshe a ranar Assabar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.