Isa ga babban shafi
Faransa

Majalisar Faransa na nazarin ayyukan Gwamnatin kasar

Majalisar Dokokin kasar Faransa ta gudanar da zama na musamman a yau talata domin jefa kuri’ar amincewa ko kuma rashin amincewa da salon siyasar Firaministan kasar Faransa Manuel Valls.  

Firaminstan kasar Faransa Manuel Valls a zayen Majalisar dokokin kasar.
Firaminstan kasar Faransa Manuel Valls a zayen Majalisar dokokin kasar. REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

Cikin jawabin da ya gabatar a gaban ‘yan Majalisar, Valls  ya ce zai ci gaba da aiwatar da sauye-sauye domin farfado da tattalin arzikin kasar Faransa,  ya kuma bukaci goyan bayan daukaci yan Majalisar wata hanyar ceto tattalin arziki kasar daga durkushewa.

Gwamnatin Faransa  na fuskantar suka daga bangarori daban-daban na  yan siyasa dama  kungiyoyin  kwadagon kasar da cewa ta kasa cika alkawuran da ta dauka a baya, ta bangarorin samarwa matasa ayyukan yi dama kawo daidaito  a fuskar tattalin arziki kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.