Tsohon Shugaban Hukumar Bada lamuni ta Duniya, Dominique Strauss Kahn, ya shigar da kara a kotu inda yake bukatar Nafisatou Diallo, matar da ta yi masa zargin yunkurin yi mata fyade a New York, ta biya shi Dala miliyan guda, saboda bata masa suna.
Shugaban Kasar Faransa, Francois Hollande, tare da takwararsa ta kasar Jamus, Angela Merkel, sun yi alkawarin aiki tare, don ganin sun magance matsalolin da ke addabar kudin euro da kuma tattalin arzikin Turai.
Yanzu Haka Nicolas Sarkozy, ya zama tsohon shugaban kasar Faransa, bayan rantsar da Hollande abinda ya kawo karshen mulkinsa na shekaru biyar da ‘Yan Faransa da dama suka yi ta korafi akai.
Mai ra’ayin gurguzu, Francois Hollande ya karbi ranstuwar shugabancin Faransa tare da bayyana fatar samar da sauyi a kasar da Nahiyar Turai. Ana sa ran Sabon shugaban zai zabi Fira Ministan kafin ya nufi zuwa kasar Jamus don tattaunawa da Angela Merkel.
Gwamnatin kasar Spain a yau juma’a ta amince da wani sabon shirin tafiyar da bankunan kasar da suka fi karkata kan sashen gidaje, inda aka umarci bankunan da su bayyana sakamakon ayukansu, da kuma umartarsu da samar da wani sabon shiri na kimanin Euro miliyan dubu 30 nan gaba.
A yau alhamis Fra Ministan kasar Fransa Francois Fillon ya gabatar da murabus din gwamnatinsa, wace zata ci gaba da tafiyar da wasu muhimman ayuka kafin zababben shugaban kasar Francois Hollande ya fara aiki a ranar talata mai zuwa, inda zai nada wata sabuwar gwamnati.
Ta Wayar Salula, Shugaban kasar Amurka Barack Obama, ya taya shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin murnar sake zama shugaba a karo na uku, bayan kwashe lokaci shugabannin biyu suna adawa da juna. Sai dai Putin yace ba zai samu damar halartar taron kasashen G8 da za’a gudanar a Amurka.
Shugaba mai jiran gado a kasar faransa, Francois Hollande da shugaban kasar mai barin gado, Nicolas Sarkozy a jiya talata sun tsaya kafada da kafada a wani taron tunawa da yakin duniya na biyu kwana uku kacal bayan zaben da aka gudanar lahadin da ta gabata.
Shugaban Jam’iyyar Syriza ta kasar Girka, Alexis Tsipras, ya yi alkawarin soke tallafin kasashen Turai da Hukumar bada Lamuni ta Duniya tare da yin watsi da shirin tsuke bakin aljihu idan ya kafa Gwamnati. Yanzu haka Jam’iyyar Syriza ta fara tattaunawa da sauran Jam’iyyu domin kafa gwamnatin hadin gwiwa.
Kwanaki bayan samun nasarar shi a zaben shugaban kasar Faransa, François Hollande zai fuskanci jerin bukatun Faransawa kafin kama aiki a fadar shugaban kasa. Babban kalubalen da ke gaban sabon Shugaban shi ne daidaita matsalar tattalin arzikin Faransa.
Vladimir Putin ya karbi rantsuwar shugabancin kasar Rasha karo na uku bayan an yi taho mu gama tsakanin Jami’an tsaro da masu zanga-zangar adawa da gwamnatin shi. Putin ya karbi rantsuwar kare ‘Yancin kasar Rasha da mutanenta Bayan ya rungume kundin tsarin mulkin kasar.
Dan takarar Jam’iyyar Gurguzu ta Socialist François Hollande ya kada shugaban kasa mai ci Nicolas Sarkozy a zaben shugaban kasar Faransa zagaye na biyu. Hollande shi ne Mutum na Farko da ya lashe zaben shugaban kasa karkashin Jam’iyyar Gurguzu tun zamanin François Mitterrand a shekarar 1988.
Hukumomin kasar Rasha, a karon farko sun bada dama ga ‘yan adawa domin gudanar da gangami a tsakiyar birnin Moscow. Wannan kuma na zuwa ne kwana daya kamin kaddamar da shugaba Vladmir Putin a wa’adi na uku.
A wata hira ta musamman da François Hollande ya yi da RFI da France 24, dan takarar shugaban kasar Faransa yace ya yaba da kokarin shi a muhawarar da ya yi da Sarkozy tare da sukar gwamnatin Sarkozy ta raba Faransawa.
Kunghiyar Tarayyar Turai ta kakabawa Jagororin juyin mulki na kasar Guinea Bissau takunkumin hana su sukuni, bayaga jerin takunkumin da Kungiyar kasashen yammacin Africa suka riga suka kakaba masu.
Shugaban Kasar Faransa, Nicolas Sarkozy, da abokin adawarsa, Francois Hollande, sun yi musayar kalamai marasa dadi a mahawarar karshe da suka gudanar yammcin jiya, kafin zabe zagaye na biyu a ...
Hankalin Jaidun Faransa a yau ya rabu gida biyu domin wasu sun mayar da hankali ne akan yakin neman zaben ‘Yan siyasa da aka gudanar a jiya ranar bukin ma’aikata, wasu kuma jaridun sun mayar da hankali ne akan muhawarar da za’a gudanar a yau tsakanin Sarkozy da Hollande a kafar Telebijin.