Wata Kungiyar fararen hula a Jamhuriyar Nijar, ta bukaci kamfanin Areva, mallakar kasar Faransa, da ke hako ma’adinin uranium a kasar, biyan kudaden Diyya ga ‘Yan Nijar dai dai da yadda Kamfanin ke biyan Faransawan da suka mutu.
Manyan Jami’an tsaron kasashen da ke raya tafkin Chadi, sun gudanar da taro a Jamhuriyar Nijar, don nazarin hanyoyin da zasu dakile safarar makamai da kuma ayyukan ta’adanci domin samun ci gaban kasashensu.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta yi watsi da rahotan kungiyar agaji ta Save the Children, wanda yace mata na fama da tsananin wahala wajen haihuwa da kuma renon kananan yara, abinda ya sa kasar ta zama ta karshe a mizanin kasashen duniya 165.
A wani sabon Rahoto game da halin rayuwar iyaye mata da hukumar kare lafiyar kananan yara ta fitar, ya nuna Nijar ce kasar da iyaye Mata ke shan wahala bayan maye gurbin kasar Afghanistan a karon farko. Kasar Norway ce a matsayin kasa ta farko da iyaye Mata ke shan dadi a jerin kasashe 165 da aka kwatanta rayuwarsu.
Gwamnatin kasar Chadi ta yi kiran kasashen 16 a kungiyar raya tafkin Chadi domin samar da dakarun hadin kai don yaki da ‘Yan kungiyar Boko Haram da ke barazana ga sha'anin tsaro a Najeriya da makwabtanta.
Babban Bankin Duniya yace tattalin Arzikin kasashen yammacin Afrika ya samu ci gaba bana. Wannan na zuwa ne saboda samun rangwame ga farashin kaya da yawaitar hannayen jari da hako ma’adanai da suka kawar da raunin fitar da kaya zuwa waje.
Shirin Lafiya Jari ya diba matsalar hunturu ga Lafiyar al'umma a kasashen Afrika tare da tattaunawa da Likita wanda ya yi bayani dangane da yadda mutum zai kare lafiyar shi ga kamuwa da cutar ...
Kungiyar kasashen Turai ta EU zata amince da kudirin tura tawagar da zata horar da sojin Jamhuriyar Nijar, don fuskantar kalubalen yaki da ta’adanci da ke yaduwa a iyakokin kasar sanadiyar rikicin kasar Libya da Mali masu makwabtaka da Nijar.
Aghali Alambo,wani tsowo shuganban yan tawaye MNJ ne, a Jamhuriyar Niger na tsaka mai wuya, bayan da hukumomin kasar ke tuwuma sa da alaka da yan ta’ada.
Shirin ya diba kokuwar gargajiyar Jamhuriyyar Nijar da aka kammala a Jahar Maradi inda Laminou Mai Dabba na Agadez ya lashe Takobin Kokuwar a bana bayan ya karba hannun Ummaru Bindigou na Maradi.
An kammala gasae kokuwar gargajiyar kasar Janhuriyar Nijar na wannan shekara ta 2012, bayan samu nasara yayin wasan karshe da aka ranar Lahadi hudu ga wan Febrairu.
A yau ne za’a bude gasar kokuwa a Jamhuriyyar Nijar a birnin Maradi, bayan fara gasar a shekarar 1975 a birnin Tawa, kuma tun a lokacin ne ake gudanar da gasar ta kokuwa duk shekara. Yanzu haka an gudanar da gasar sau 31 bayan kammala gasar a bara a birnin Tliberi.
Akalla ‘Yan gudun hijira 35,000 suka tsere daga kasar Mali zuwa kasashen Burkina Faso da Nijar, don samun mafaka sanadiyar rikicin da ake ci gaba da gudanarwa tsakanin ‘Yan tawayen Tuareg da dakarun Gwamnati.
A cikin shirin, mun diba irin matsalolin da suka shafi Tawagar ‘Yan wasan Mena a gasar cin kofin Åfrika da aka kammala a kasashen Gabon da Equatorial Guinea da irin matsalolin da suka shafi kwallon kafa a Najeriya da sabbin sauye sauye da kasar ke yi domin kaucewa bacin rana.
Shugabannin kwamitin Tallafi na Majalisar Dinkin Duniya da Kungiyar Tarayyar Turai sun nemi kasashen duniya bayar da tallafin gaggawa, domin shawo kan matsalar yunwa da ke addabar yankin Sahel na yammacin Afrika, inda suka bayyana cewa ana bukatar kudi Dalar Amurka miliyan 725 a bana.
Shugabanin kasashen Afrika ta Yamma, na kungiyar ECOWAS, zasu gudanar da taronsu a Abuja, inda ake saran zasu zabi sabon shugaba, saboda kawo karshen wa’adin Shugaba Goodluck Jonathan na Najeriya.