Watakila matsalar wutar lantaki zata tabarbare a Najeriya
Hukumomi a Najeriya sun bayyana cewa yau Asabar, matsanaciyar matsalar wutar lantarkin da ake fuskanta a kasar zata kazance, in har yajin aikin da ma’aikan kamfani mai suke yi ya ci gaba. Wani babban jami’a a ma’aikatar wutar lantarkin kasar Godknows Igal, yace kafin wannan matasalr da ake fuskata ta rashin wadataccen mai, kasar na samar da wutar lantarkin da ta kai Megawatt 4,800, amma yanzu ta ragu zuwa 1,300.Jamin yace lamarin zai iya tabarbarewa in har yajin aikin ma’aikatan man ya ci gaba.A halin da ake ciki dai, wasu sasan kasar ta Najeriya an shafe kwanaki, wasu wuraren ma makonni ba wutar ta lantarki, lamarin da ya jefa harkokin kasuwanci a matsala.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: