Isa ga babban shafi
Najeriya

Mutane 37 suka mutu a hare haren Kano da Potiskum

Akalla mutane 37 aka tabbatar da mutuwarsu a hare haren kunar bakin wake guda biyu da aka kai a tashar mota a biranen Kano da Potiskum a arewacin Najeriya. cikin sa’I’o kalilan ne aka kai hare haren a ranar Laraba a yayin da ya rage saura makwanni biyar a gudanar da babban zabe a kasar.

Harin da aka kai a tashar Motar Kano Line
Harin da aka kai a tashar Motar Kano Line RFI Hausa/Dandago
Talla

Mutane 17 suka mutu a harin farko da aka kai a tashar Motar Dan-Borno a garin Potiskum, sama da 30 ne kuma suka samu rauni.

Bayan sa’o’I kalilan ne kuma wasu ‘yan kunar bakin wake guda biyu suka tayar da bom a tashar motar Kano Line.

Wakilin RFI a Kano Abubakar Issa Dandago ya ce ‘Yan kunar bakin waken sun tayar da bom din ne a cikin mota kirar Golf.

Amma rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano tace mutane 12 ne suka mutu.

01:35

Rahoton Harin kunar bakin wake a Kano Line

Abubakar Issa Dandago

Wannan dai shi ne hari na farko da aka kai a Kano a 2015 bayan hare haren baya da aka kai inda aka samu hasarar rayukan mutane da dama.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.