Isa ga babban shafi
Ilimi Hasken Rayuwa

Idris da ya kera jirgi ya sake kera lemar tashi sama a Kano

Wallafawa ranar:

Shirin Ilimi Hasken Rayuwa ya tattauna ne game da lemar da ke tashi sama da mutum da ake kira Paramotor a turance, wanda wani matashin garin Kano Idris Ibrahim Hassan ya samar bayan ya kera jingin sama a watannin da suka gabata.

Idris Ibrahim yana kokarin tashi sama da Paramoton da ya  kera a  filin sukuwa a Kano
Idris Ibrahim yana kokarin tashi sama da Paramoton da ya kera a filin sukuwa a Kano RFI Hausa/Awwal
Talla

An dade dai da samar lemar da ake amfani da ita a diro daga jirgin sama wacce ake kira ‘Parachute’, daga baya ne kuma aka samar da Paramotor mai dauke da inji da fanka da kuma lemar da mutum zai rataya a baya ya tashi sama daga kasa.

Bidiyo

Shirin ya tattauna da Idris wanda ke ci gaba da aikin kere kerensa na fasahar ababen hawa da ke tashi sama. Kuma a cikin Shirin Idris ya yi bayani game da dalilin kera Paramoto da kuma amfanin shi ga al’umma.

Paramoto da Idris ya kera a Kano

Idris yana gudanar da ayyukan kere kerensa na fasaha da kudin aljihunsa, kuma yace babban abin da ya ke nema a yanzu shi ne tallafin daukar nauyin karatunsa a fannin kirar jiragen sama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.