Najeriya
Kauracewa komawa makarantu a Najeriya
Kungiyar Malaman makarantu a Najeriya ta sanar da shirin kauracewa bude makarantun da ake shirin yi ranar litinin mai zuwa saboda abinda suka kira rashin horar da jami’an su kan yadda za’a magance cutar ebola.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Shugaban kungiyar Michael Olukoya ya bukaci ya'an kungiyar su kaucewa makarantu ranar litinin har sai sun samu horarwa da ta kamata da kuma kayan aiki.
Da dai an shirya bude makarantun ne ranar 22 ga watan da ya shude bayan wani zaman taron Ministan ilimi da kwamishinonin Jihohi da kuma takwarorin su na lafiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu