Najeriya

Syndicate contentNAJERIYA
Gungun mata da Amaren da aka daurawa aure a Kano
16/05/2012 - Najeriya

Hisbah ta daura auren Zawarawa 100 a Kano

Hukumar Hisbah a Jihar Kano, ta daura wa Zawarawa 100 aure cikin 1,000 da aka shirya yi, dan magance mace macen aure a Jahar.

Tsohon Sarkin Gwandu, Mustapha Haruna Jokolo
16/05/2012 - Bakonmu a Yau

Tsohon Sarkin Gwandu, Mustapha Haruna Jokolo

A hirar shi da Rediyo Faransa, Mai Martaba Sarkin Gwandu mai Murabus, Manjo Mustapha Haruna Jokolo kuma Tsohon Dogarin Janar Muhammadu Buhari, yace babu wani ci gaba da shugabannin Arewa suka tsinanawa yankin bayan kwashe shekaru ‘Yan arewa na mulki a Najeriya. Jokolo yace ci gaban da gwamnatin su Sardauna suka samar a Arewa yanzu sai dai Tarihi.

Shirin mayar da Makarantun Allo karkashin Gwamnatin Najeriya
16/05/2012 - Ilimi Hasken Rayuwa

Shirin mayar da Makarantun Allo karkashin Gwamnatin Najeriya

Shirin Ilimi Haske Rayuwa ya sake diba batun yunkurin mayar da makarantun Allo karkashin Gwamnati a Najeriya, wanda Malaman Zaure ke suka.

Taswirar kasar Guinea Bissau da kasashen da ke makwabtaka da kasar
15/05/2012 - ECOWAS-Guinea Bissau-Najeriya

Najeriya zata tura dakarunta zuwa Guinea Bissau

Gwamnatin Najeriya tace zata girke dakarunta a kasar Guinea Bissau don taimakawa kasar komawa ga mulkin fararen hula, kamar yadda kungiyar ECOWAS ta bukata.

Zanga zangar lumana, saboda neman hukunta masu hannu a badakalar mai a Nigeria
14/05/2012 - Tattaunawa

Zanga zangar lumana, saboda neman hukunta masu hannu a badakalar mai a Nigeria

A yau shirin na mu zai ji ra’ayoyinku ne a akan zanga zanagar lumunar da kungiyoyin farar hula su ka ca zasu gudanar domin jinkirin da gwamnatin tarayya ke yi wajen cafke wanda a aka sami ...

wani mahaki darma a jahar Zamfara
11/05/2012 - Nigeria

Yara na cikin kasadar shakar gubar dalma

KUNGIYAR likitoci ta duniya Doctors Without Borders tace fiye da yara kanana dubu dubu daya da dari 5, sun shaki gubar dalma a kauyen Bajega da ke jihar zamfara a taraiyyar Nigeria.

11/05/2012 - Nigeria

An mayar wa alkalin kotun daukaka karar Nigeria mukamin shi

Hukumar kula da lamuran Shari’ah a Nigeria ta dawo da alkalin kotun daukaka karar kasar, mai shari’ah Ayo Salami kan mukamin shi.

Shugaban Cote d'IVoire Alassane Ouattara kuma shugaban ECOWAS a lokacin da yake ganawa da Goodluck Jonathan na Najeriya a filin saukar jirgi na Felix Houphouet Boigny a Abidjan
10/05/2012 - ECOWAS-Guinea Bissau-Najeriya

ECOWAS zata tura Tawaga zuwa G/Bissau, inji Goodluck

A wata ziyara da kai kasar Cote d’Ivoire, Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, yace kungiyar kasashen Afrika ta Yamma, ECOWAS, zata tura wata tawaga zuwa kasar Guinea Bissau don tattaunawa da sojojin kasar, domin ganin sun mayar da kundin tsarin mulki.

Garken Rakuma suna sha ruwa a gabar Tabkin Chadi da ke kewaye da tsaunuka
09/05/2012 - Nijar-Najeriya-Chadi

Kasashen raya tabkin Chadi zasu samar da dakarun hadin gwiwa don yaki da Ta’addanci

Manyan Jami’an tsaron kasashen da ke raya tafkin Chadi, sun gudanar da taro a Jamhuriyar Nijar, don nazarin hanyoyin da zasu dakile safarar makamai da kuma ayyukan ta’adanci domin samun ci gaban kasashensu.

Dakta Muhammed Ali Pate
09/05/2012 - Bakonmu a Yau

Dakta Muhammed Ali Pate

Ma’aikatan Lafiya a Najeriya sun tsunduma cikin yajin aikin gama-gari, saboda kin biya musu bukatun su da Gwamnatin kasar ta yi. Wannan kuma na zuwan ne kwana daya da korar Likitoci kusan 800 da gwamnatin Lagos ta yi saboda yajin aikin da suka kwashe makwanni suna gudanarwa saboda neman karin karin albashi. Dakta Muhammed Ali Pate shi ne Ministan Lafiya kuma ya yi bayani daga bangaen gwamnati.

kofar shiga Jami'ar Bayero  da ke Kano
08/05/2012 - Najeriya

Wani bom ya tashi a Kwalejin ilimi da ke Kano

Rahotanni daga Kano a Nigeria na cewa wani bom ya tashi a Kwalejin Ilimi da ke birnin Kano.

Matan kasar Afghanistan a lokacin gudanar da bukin ranar mata a yankin Ghazni a ranar 8 ga watan Maris
08/05/2012 - Lafiya

Kasar Norway ne iyaye mata suka fi shan dadi amma a Nijar suka fi shan wahala

A wani sabon Rahoto game da halin rayuwar iyaye mata da hukumar kare lafiyar kananan yara ta fitar, ya nuna Nijar ce kasar da iyaye Mata ke shan wahala bayan maye gurbin kasar Afghanistan a karon farko. Kasar Norway ce a matsayin kasa ta farko da iyaye Mata ke shan dadi a jerin kasashe 165 da aka kwatanta rayuwarsu.

Likitocin Najeriya a Jahar Legas lokacin da suke maci domin neman biyansu kudaden Albashi
08/05/2012 - Najeriya

Gwamnatin Jahar Legas a Najeriya ta kori Likitoci 788

Hukumomin Jahar Legas a Najeriya sun tabbatar da sallamar Likitoci 788 wadanda ke yajin aiki tsawon makwanni uku. Gwamnatin Jahar Legas tace yajin aikin Likitocin ya sabawa doka.

Yajin aikin likitoci a Nigeria da korar likitoci a Lagos
08/05/2012 - Tattaunawa

Yajin aikin likitoci a Nigeria da korar likitoci a Lagos

GWAMNATIN Jihar Lagos a Nigeria, ta sanar da korar likitoci 788 daga aiki, saboda kin amsa takardun tuhumar da aka musu na zuwa yajin aiki.

MD Abubakar Sabon Sufeto Janar na 'Yan sandan Najeriya
07/05/2012 - Najeriya

Har yanzu ana zaman dar-dar a Potiskum

Rahotanni daga garin Potiskum dake jihar Yobe a Nigeria na cewa hankulan matasan garin ya tashi matuka sakamakon zargin da sukeyi, wa jami'an tsaron hadin guiwa dake garin, na hannu tsundum ...

'Yan Acaba a Najeriya
07/05/2012 - Najeriya

Gwamnatin Flato a Najeriya ta haramta yin Acaba

Gwamnatin Jahar Flato a Najeriya ta sanar da haramta yin Acaba da babura a birnin Jos da kewaye, saboda yunkurin dakile ayyukan laifi da ake da baburan, kamar yadda ta sanar bayan taron Majalisar ...

Rashidi Yekini na Najeriya ya mutu yana da shekaru 48
07/05/2012 - Wasanni

Rashidi Yekini na Najeriya ya mutu yana da shekaru 48

Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon ya yi bayani ne game da Rashidi Yakini tsohon dan wasan Super Eagle a Najeriya wanda Allah ya yi wa rasuwa a ranar Juma’a 4 ga watan Mayu yana da shekaru 48 bayan kwashe lokaci yana jinyar rashin lafiya.

Tattaunawar karshen Mako akan cika shekara Biyu da Mutuwar Yar'adua
05/05/2012 - Tattaunawa

Tattaunawar karshen Mako akan cika shekara Biyu da Mutuwar Yar'adua

Shirin Tattaunawar karshen Mako ya yi bayani ne game da cika shekara Biyu da mutuwar tsohon shugaban Najeriya Ummaru Musa 'Yar'adua.

03/05/2012 - Nigeria-Yobe-Hari-Kasuwa

Akalla sama da mutane 34 zuwa 50 ne suka rasa rayukansu a wani hari a kasuwar Patiskum a jahar Yobe

A kalla mutane 34 ne suka rasa rayukansu a cikin wani harin Bam da aka kai a wata kasuwa dake garin Patiskum na jahar Yobe, a yankin arewacin tarayyar Nigeriya, kamar yadda majiyoyin gwamnatin jahar Yobe, da na shaidun gani da ido suka tabbatar, inda aka bayyana cewa, yawan mutane da suka rana rayukansu na iya karuwa.

Harin Ginin Kamfanin Jaridar thisday a Abuja Najeriya bayan kai hari
02/05/2012 - Najeriya

Harin This Day: Boko Haram ta yi gargadin sake kai wa kafafen yada labarai hari

Kungiyar Jama'atu Ahlus Sunnah Lidda'awati wal Jihad da aka fi sani da sunan Boko Haram a Najeriya, ta fitar da Wani hoton Bidiyo mai dauke da bayanin harin Ofishin Jaridar This Day tare da yin barazanar ci gaba da kai wasu hare hare a manyan kafafen yada labarai da ma'aikatansu a kasar.

Close