Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta yi watsi da rahotan kungiyar agaji ta Save the Children, wanda yace mata na fama da tsananin wahala wajen haihuwa da kuma renon kananan yara, abinda ya sa kasar ta zama ta karshe a mizanin kasashen duniya 165.
A wani sabon Rahoto game da halin rayuwar iyaye mata da hukumar kare lafiyar kananan yara ta fitar, ya nuna Nijar ce kasar da iyaye Mata ke shan wahala bayan maye gurbin kasar Afghanistan a karon farko. Kasar Norway ce a matsayin kasa ta farko da iyaye Mata ke shan dadi a jerin kasashe 165 da aka kwatanta rayuwarsu.
Likitoci a kasar Pakistan sun ce sun samu nasarar ceto rayuwar wani jariri da aka Haifa da kafa Shida a kasar bayan an yi masa aikin tiyata inda aka cire kafa hudu daga Shida.
Hukumar tantance magani a kasar Amurka zata yanke hukunci a watan Yuli game da kwayar magani ta Qnexa da za’a sha a rage kiba. Wanda kamfanin samar da kwayar magani na VIVUS ya samar.
Masana masu binciken magungunan Bil-adama a Cibiyar Binciken Cutar Sankara ta Jami’ar Texas, kasar Amurka sun gano wasu sabbin magunguna da ke iya rage kibar jiki na mutane ba tare da illa ba.
Yayin da ya rage makonni biyu a gurfanar da tsohon shugaban kasar Masar Hosni Mubarak a gaban kotu, sai gidan talibijin din kasar ya bayar da sanarwar cewa tsohon shugaban baya cikin hayyacinsa, lamarin ka iya jefa shari’ar da ake masa cikin halin rashin tabbas.
SAKATARE Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki Moon, ya bukaci Gwamnatocin kasashen duniya, da su dauki matakan bunkasa lafiyar mata, dan cimma kudirin Majalisar na rage mace mace.