Isa ga babban shafi
Wasanni

Kungiyoyi zasu gabatar da 'yan wasa 26 a gasar nahiyar Turai ta bana

Hukumar shirya gasannin kwallon kafar Turai ta dan yi sauyi kan yawan adadin ‘yan wasa da zasu shiga tawagogin gasar neman cin kofin nahiyar ta wannan shekara.

Sabon shugaban hukumar kwallon kafar Turai Alexander Ceferin, lokacin da yake gabatar da logo "UEFA na wasan Euro 2020 a Rome",ranar 21 ga watan Saptumbar 2016.
Sabon shugaban hukumar kwallon kafar Turai Alexander Ceferin, lokacin da yake gabatar da logo "UEFA na wasan Euro 2020 a Rome",ranar 21 ga watan Saptumbar 2016. ANDREAS SOLARO AFP/Archives
Talla

Sabon tsarin UEFA ya baiwa Kowacce tawagar kwallon kafa da za ta buga gasar cin kofin nahiyar Turai ta bana, damar zuwa da 'yan wasa 26, maimakon 23 da aka saba a baya.

Hukumar ta yi wannan sauyin ne don ragewa ‘yan wasa gajiya bayan buga wa kungiyoyinsu wasanni kusa da juna, sakamakon bullar cutar korona.

Matakin zai taimakawa masu horar da tawagogin samun saukin zabin 'yan wasa koda annobar ta shafi  wata tawaga.

An kuma amince kowacce tawaga ta sauya 'yan wasa biyar-biyar a kowacce karawar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.