Spain zata lashe kofin duniya a Brazil-Hasashe
Wata cibiyar da ke sa ido ga sha’annin kwallon kafa a kasar Switzerland, ta yi fashin baki akan cewa kasar Spain ce zata lashe kofin gasar cin kofin duniya, saboda zubin zaratan ‘Yan wasan da kasar ta tara. Kuma a cikin sharhin na cibiyar tace Spain da Brazil ne za su kai ga zagayen karshe, amma Spain ce zata lashe kofin.
Wallafawa ranar:
Cibiyar CIES Football Observatory tace ta yi nazari akan dukkanin kasashen da zasu haska guda 32, kuma sakamakon binciken ya nuna cewa Spain ce zata doke Brazil a wasan karshe, sai Argentina a matsayi na uku, Faransa kuma a matsayi na hudu.
A cikin hasashen, cibiyar da ke nazarin kwallon kafa tace Faransa ce zata yi waje da Najeriya a zagaye na biyu, kamar yadda Portugal zata kori Rasha.
Kasar Spain dai zata yi kokarin kare kofin gasar ne da ta lashe a Afrika ta kudu, wanda a tarihin gasar kuma babu wata kasa da ta iya kare kofin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu