Isa ga babban shafi
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Yadda takunkuman ECOWAS kan Nijar ke haifawa 'yan kasa asara

Wallafawa ranar:

Kusan watanni uku, motoci kusan dubu biyu dauke da kayayyaki na ci gaba da kasancewa kan iyakar Nijar da Jamhuriyar Benin bisa umurnin kungiyar Ecowas. Mafi yawan motocin dai na dauke ne da kayayyakin ‘yan Nijar, yayin da wasu ke kan hanyarsu ta zuwa Mali ko kuma Najeriya, dauke da kayayyakin da ke iya lalacewa. 

Manyan motoci yayin da suka yi jerin gwano akan iyakar Najeriya da Nijar.
Manyan motoci yayin da suka yi jerin gwano akan iyakar Najeriya da Nijar. © Daily Trust
Talla

Shin ko akwai wata hujja da Ecowas ta dogara da ita domin hana ‘yan kasuwa da kuma masu motocin sufuri gudanar da harkokinsu na yau da kullum saboda an yi juyin mulki a wata kasa? 

Wace illa wannan mataki ke iya haifar wa tattalin arzikin kasashen na Yammacin Afirka baki daya? 

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Murtala Adamu...

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.