Likitoci sun tsunduma yajin aiki a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 15:46
Kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta Najeriya ta tsunduma yajin aikin gargadi na kwanaki 5 a wani yunkuri na tilastawa gwamnatin kasar biya mata wasu daga cikin alkawurran da ta daukar mata tsawon lokaci.
Wasu daga cikin bukatun da kungiyar liktocin ke son gwamnati ta biya mata har da karin kashi 200 na albashinsu baya ga janye dokar da ke Shirin tilastawa likitoci aikin akalla shekaru 5 a cikin Najeriya gabanin samun sukunin fita aiki ketare.
Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Nasiru Sani ya gabatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu