Takunkuman ECOWAS sun durkusar da matan Nijar da ke fatauci zuwa ketare
Wallafawa ranar:
Kunna - 10:00
Shirin Rayuwata na wannan rana tare da Zainab Ibrahim, ya mayar da hankali kan yadda matsin rayuwa a Jamhuriyyar Nijar ke tilastawa mata rungumar sana'o'in da bisa al'ada ba a saba ganin jinsin na Mata na yi ba.
A shekarun baya-bayan nan dai, ana ganin yadda 'yan kasuwa mata a Nijar ke gudanar da fatauci a kasashe daban-daban da suka kunshi, makwabta irinsu Najeriya da Kamaru da Chadi baya ga Saudi Arabiya da kuma birnin Dubai na hadaddiyar daular larabawa.
A cikin wannan shiri za ku ji yadda takunkuman da aka kakabawa kasar bayan juyin mulkin Soji, kai tsaye ya shafe yanayin kasuwancin matan dama tattalin arzikinsu.
Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu