Isa ga babban shafi
Rayuwata

Najeriya na cikin kasashen da suka fi fama da mutuwar jarirai a duniya

Wallafawa ranar:

Najeriya ta kasance kasa ta biyu a jerin kasashen da ke fama da matsalar mutuwar jarirai yayin haihuwa a duniya, kamar yadda kwararru daga Cibiyar Nazarin Halittar Dan Adam ta Najeriya ta bayyana. 

Hukumomin kiwon lafiya a duniya na ganin cewa ya kamata a dauki matakin gaggawa, kan yadda za a magance wannan matsala, musamman a matalautan kasashe.
Hukumomin kiwon lafiya a duniya na ganin cewa ya kamata a dauki matakin gaggawa, kan yadda za a magance wannan matsala, musamman a matalautan kasashe. DIDIER PALLAGES / AFP
Talla

Kwararrun sun bayyana hakan ne a birnin Abuja yayin wani taron hadin gwiwa na masu ruwa da tsaki kan inganta shirin kula da lafiya a Najeriya bisa bayanan mutuwar jarirai da aka samu.

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin Rayuwata tare da Zainab Ibrahim

Rahoton ya ce kididdigar da aka samu kan mutuwar jarirai yayin haihuwa a Najeriya ya haura kashi 46 cikin 100 a cikin 1,000 da aka haifa.

Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya fitar da rahoton da ke nuna cewa Najeriya ta sami yawan  mace-macen jarirai da kashi 42.9 a shekarar 2021, wanda hakan ya sanya ta kasance a matsayi ta biyu a tsakanin kasashen da ke da fama da wannan matsala a duniya

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
  • 10:00
  • 10:00
  • 10:00
  • 10:00
  • 10:00
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.