Mu Zagaya Duniya
Shirin Mu Zagaya Duniya na duba Wasu Muhimman Labarai da suka ja hankalin Duniya a cikin mako. Ana gabatar da shirin ne a ranar Asabar da safe a kuma maimaita ranar Lahadi da daddare.
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
Daukacin kashi-kashi
-
Gwamnatin Najeriya ta haramta karbar shaidar karatun digiri daga Benin da Togo
Daga cikin labarun da shirin 'Mu Zagaya Duniya' ya sake waiwaya a wannan makon akwai matakin da gwamnatin Najeriya ta dauka na haramta karbar takardun shaidar kammala karatun digiri daga jami'o'in Jamhuriyar Benin da kuma kasar Togo.15/01/202419:45 -
Bitar wasu muhimman labaran da suka faru a duniya cikin wannan mako
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai batun yadda yan ta'adda a Najeriya ke gina ramu suna boyewa, saboda barin wutar da suke sha daga sojojin kasar, sai kuma batun kammala ficewar sojojin Faransa a Nijer da dai sauran manyan labaran da suka hada da Burkina Faso, jamhuriyar Benin, yakin Isra'ila da Hamas, tare da dokar yan ci rani da Faransa ta amince da ita.23/12/202320:04 -
ECOWAS/CEDEAO ta tabbatar da juyin mulki aka yi a Nijar
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai matakin da kungiyar kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ko CEDAEO ta dauka na amincewa da da cewar an yi juyin Mulki a Nijar, sannan kuma ta dakatar da ita daga cikin ta har sai lokacin da sojoji suka maida wa farar hula Mulki.A Najeriya kuma, Bankin Duniya ne ya bukaci gwamnatin kasar ta fadada tsauraran matakan da take dauka na yi wa tattalin arzikin kasar garambawul, domin ceto shi daga durkushewa baki daya a nan gaba.16/12/202320:31 -
COP28 - An samar da asusun tallafa wa kasashe don yaki da matsalar sauyin yanayi
Shirin "Mu zagaya duniya" na wannan makon tare da Khamis Saleh ya waiwari babban taron sauyin yanayi na COP28 da aka faro a Dubai, inda aka samar da wani asusu na musamman da manyan kasashe za su rinka zuba kudi don taimaka kananan kasashen da matsalar da ba su suka samar ba ta fi shafa.02/12/202319:46 -
Bitar wasu daga cikin labaran da suka dauki hankali na mako
Shirin zai kuma waiwayi kalaman da tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo yayi kan cewa Dimokaradiyar kasashen yammacin turai fa ba ta haifa wa nahiyar Afirka da mai idanu ba.25/11/202319:50 -
MU zagaya Duniya: Kotun daukaka kara a Najeriya ta soke zaben gwamnan jihar Kano
Ciki Shirin wannan makon za a ji cewar Kotun Daukaka karar Najeriya ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben Kano da ya karbe kujerar Gwamnan jihar daga hannunn Abba Kabir Yusuf na NNPP ya mika ta zuwa Nasir Yusuf Gawuna na APC.Kasar Ghana ta bukaci hadin gwiwar kasashen Afirka domin tilasta wa kasashen da suka yi wa nahiyar mulkin mallaka biyansu diyya akan yadda suka azabtar da su da cinikin bayi.18/11/202319:55 -
wasu daga cikin muhimman lamurran da suka wakana a wannan makon
Halin da asibitoci ke ciki a Zirin Gaza, bayan da aka shafe sama da wata guda Isra’ila na ci gaba da ruwan bama-bamai kan Falasdinawa, wadanda ya zuwa yanzu akalla dubu 40 suka jikkata baya ga sama da 10 da suka mutu a Gaza tareda Nura Ado Suleiman.11/11/202319:58 -
Isra’ila ta kashe Falasdinawa sama da dubu 9,000, fiye da rabinsu kuma mata ne da kananan yara
Majalisar Dinkin Duniya, ta bukaci a gaggauta tsagaita wuta a Zirin Gaza, tare da gargadin cewa lokaci na kurewa kasashe kan bukatar dakile yi wa Falasdinawa kisan kare dangi a yankin na Gaza.04/11/202320:05 -
Muhimman labarun lamurran da suka wakana a cikin mako
Rundunar sojin Isra’ila ta ce dakarunta sun kai farmakin wucin gadi a arewacin yankin Zirin Gaza ta kasa a cikin daren ranar Alhamis, inda suka yi arrangama da mayakan Hamas a matsayin sharar fagen shirinta na kaddamar da gagarumin farmakin murkushe kungiyar ta Hamas28/10/202320:03 -
Harin asibitin Gaza ya janyo cece-ku-ce
Cikin labarun da shirin makon nan ya waiwaya akwai Harin da ya kashe daruruwan mutane a babban asibitin Zirin Gaza, lamarin da fusata kasashe da dama, da hukumomi, da kungiyoyin na kasa da kasa, da sauran al’umma a sassan duniya. Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sanar da dakile wani yunkurin hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum na tserewa daga gidan da ake tsare da shi.21/10/202318:26 -
Halin da ake ciki a Zirin Gaza bayan barkewar yaki tsakanin Isra'ila da Hamas
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' da ya saba waiwayar labarun makon da ya kare a wannan karon ya mayar da hankali kan yakin da ya barke tsakanin Isra'ila da mayakan Falasdinawa na kungiyar Hamas.14/10/202319:59 -
Mu zagaya Duniya
Masu sauraro Assalamu alaikum, barkanmu da sake haduwa cikin Shirin Mu Zagaya duniya daga nan sashin Hausa na Radio France International RFI………Nura Ado Suleiman zan jagoranci bitar wasu daga cikin muhimman labarun lamurran da suka wakana a makon da ya gabata.07/10/202318:56 -
Shirin Mu Zagaya Duniya
Masu sauraro Assalamu alaikum, barkanmu da sake haduwa cikin Shirin Mu Zagaya duniya daga nan sashin Hausa na Radio France International RFI………Nura Ado Suleiman zan jagoranci bitar wasu daga cikin muhimman labarun lamurran da suka wakana a makon da ya gabata.30/09/202319:51 -
Bitar labaran mako- 'Yan bindiga sun yi awon gaba da tarin daliban jami'ar Gusau
Shirin Mu zagaya duniya tare da Nura Ado Suleiman kamar kowanne mako ya yi bita ne kan muhimman labaran da suka faru a makon da muka yi bankwana da shi, inda a cikinsa za ku ji yadda 'yan bindiga suka sace gomman dalibai a Jami'ar tarayya ta birnin Gusau a jihar Zamfara.23/09/202320:07 -
Mu Zagaya Duniya
Shirin Mu Zagaya Duniya na duba Wasu Muhimman Labarai da suka ja hankalin Duniya a cikin mako. Ana gabatar da shirin ne a ranar Asabar da safe a kuma maimaita ranar Lahadi da daddare.16/09/202320:02
Mu Zagaya Duniya
Shirin Mu Zagaya Duniya na duba Wasu Muhimman Labarai da suka ja hankalin Duniya a cikin mako. Ana gabatar da shirin ne a ranar Asabar da safe a kuma maimaita ranar Lahadi da daddare.