Isa ga babban shafi
RAHOTO

Rundunar sojin Najeriya ta dauki alhakin harin da ya kashe masu maulidi a Kaduna

A Najeriya gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da tabbacin cewa ko shakka babu jirgin sojin kasar ne ya yi barin wuta kan masu bikin mauludi, a kauyen Tudun Biri na karamar hukumar Igabi, bisa zargin ‘yan ta’adda ne wanda ya kai ga kisan mutane akalla 30.

Gwamnatin jihar ta ce za ta biya diyya ga iyalan mutanen da lamarin ya rutsa da su.
Gwamnatin jihar ta ce za ta biya diyya ga iyalan mutanen da lamarin ya rutsa da su. © Premiumtimes
Talla

Tuni dai gwamnatin jihar ta sha alwashin biyan diyyar dukkanin wadanda suka mutu a ibtila’in dama wadanda suka jikkata.

Amma rundunar sojin saman kasar, ta fitar da sanarwar cewa, bata da hannu a harin bam din da ya kashe mutane da dama a kauyen.

Kakakin rundunar, Air Commodore Edward gabkwet, ya lura da cewa basu da masaniya a harin da aka gudanar cikin sa'o'i 24 da suka gabata.

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken rahoton Aminu Sani Sado.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.