Sojin Nijar za su iya mika mulki cikin watanni 9 - Tinubu
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce idan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar suna da gaskiya, a cikin watanni 9 suna iya shirya zaben da za a mayar da mulki ga gwamnatin farar hula kamar yadda aka yi lokacin mulkin Janar Abdusalami Abubakar a Najeriya bayan mutuwar Sani Abacha.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Tinubu wanda yake jawabi lokacin da ya karbi tawagar shugabannin Musulmin Najeriya a karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, Muhammad Saad Abubakar, ya ce juyin mulkin da aka yi a Nijar shi ya bude kofar wanda ya faru a kasar Gabon.
Shugaban ya ce a matsayin Najeriya na makociyar Nijar, ba za ta taba barin dangantakarsu ta katse ba, yayin da yake cewa babu wanda yake bukatar zuwa yaki saboda ganin irin illar da yakin ya haifar a kasashen Ukraine da Sudan, amma kuma ya zama wajibi a dauki mataki mai karfi domin kauce wa illar da matakin zai haifar.
Shugaban ya roki Sarkin Musulmi cewar ya zama wajibi ya koma Nijar domin sake ganawa da sojojin da suka yi juyin mulkin, saboda abin da suka yi ya saba ka’ida, inda ya kara da cewar da zaran sun yi abin da ya dace, za su janye takunkumin karya tattalin arzikin da ke wahalar da talakawan kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu