Isa ga babban shafi

Ginin babban Masallacin Zazzau ya rufta kan masallata

Akalla Masallata hudu sun rasa rayukansu, yayin da wasu jikkata bayan ginin babban Masallacin kofar fadar sarkin Zazzau ya rufta musu.

Kofar shiga Fadar Masarautar Zazzau
Kofar shiga Fadar Masarautar Zazzau © Daily Nigerian
Talla

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Mallam Ahmed Nuhu Bamalli ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa, lamarin ya rutsa da Masallatan ne a daidai lokacin da suke gudanar da sallar la'asar da misalin karfe hudu na yamma.

Sarkin ya bayyana cewa, tun jiya aka lura da tsagewar bangon masallacin, inda kuma ake shirin kawo kwararrun injiniyoyi domin gyaran garun, yayin da wannan tsautsayi ya faru a Juma'ar nan gabanin aiwatar da gyaran.

Tuni Sarkin na Zazzau ya mika sakon ta'aziya ga iyalan mamatan, sannan ya bada umarnin ci gaba da gudanar da salla a wajen harabar Masallacin kafin kammala gyara.

Za a gudanar da sallar jana'izar mutanen da suka rasun da misalin karfe 8 da rabi na dare a fadar sarkin na zazzau da ke Kaduna a Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.