Isa ga babban shafi

Mutane 4 suka mutu a wata arangama tsakanin jami'an tsaro da 'yan Shi'a a Kaduna

Akalla mutane 4 ne ake zargin sun mutu a wata arangama tsakanin mabiya akidar Shi’a da kuma jami’an tsaron tawagar gwamnan jahar Kaduna da ke Najeriya Malam Nasiru El-Rufa’I a yankin Bakin Ruwa.

Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai.
Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Wani shaidar gani da ido ya shaidawa jaridar Daily Trust da ake wallafawa a kasar cewar, anyi arangamar ne a lokacin da ‘yan Shi’an ke gudanar da tattaki, inda wasu daga cikin su suka fara yiwa tawagar gwamnan ihu da jifa da duwatsu lamarin da ya sanya jami’an tsaro yin harbi.

Daya daga cikin jagororin ‘yan shi’a a jahar Abdullahi Usman, ya ce wadanda aka kashe ba mambobin su bane face direbobin motocin haya.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jahar Kaduna DSP Mohammed Jalige ya tababtar da faruwar lamarin sai dai ya ce suna gudanar da bincike akai.

Wannan dai ba shine karo na farko da ake samun arangama tsakanin jami'an tsaro da mabiya akidar Shi'a a jahar Kaduna, domin ko a watan Disambar shekarar 2015 sai da aka samu rikici tsakanin sojoji da su a birnin Zaria.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.