Isa ga babban shafi

Yadda ake gane alamomin cutar da ke kashe mutane a Kano

Mahukunta a jihar Kano da ke Najeriya na ci gaba da fadakar da jama’a game da alamomin wata nau’in cuta mai saurin kisa da yanzu haka ta bulla a wasu sassan Jihar. Daga cikin alamomin wannan cuta har da zubar majina daga hanci da tari babu kakkautawa da zazzabi da kuma ciwon makoshi.

Cutar ta fi kama kananan yara a cewar hukumomin kiwon lafiya.
Cutar ta fi kama kananan yara a cewar hukumomin kiwon lafiya. AFP - DJIMET WICHE
Talla

Ya zuwa yanzu, cutar da ake kiran ta 'diptheria' a harshen Turanci ko kuma mashako a Haussa, ta halaka kusan mutane 30, baya ga wasu da dama da ke kwance a asibiti. 

Tuni dai aka bude wuraren killlace wadanda suka kamu da cutar don magance bazuwarta. 

Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken rahoton Abubakar Isa Dandago daga birnin Kano

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.