Isa ga babban shafi

Najeriya: 'Yan sanda sun ceto masunta 28 a hannun 'yan fashin teku a Akwa Ibom

‘Yan sanda a jihar Akwa Ibom da ke kudu maso kudancin Najeriya sun ceto wasu masunta 28 daga hannun ‘yan fashin teku da suka yi garkuwa da su bayan sun sace su a yayin da suke bakin aiki.

Wasu jami'an tsaron Najeriya.
Wasu jami'an tsaron Najeriya. AP - Sunday Alamba
Talla

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Olatoye Durosimi ne ya bayyana haka yayin da yake gabatar da jawabi ga manema labarai a jiya Juma’a.

Ya ce yana samun wannan labarin yin ya yi maza ya umurci dakarunsa da ke aikin sintiri a ruwa da su ceto so, kuma ba su bata lokaci ba wajen kwato mutanen a hannun masu garkuwa.

Kwamishinan ya ce wadannan ‘yan fashin teku suna sajewa ne da masu kamun kifi suna aikata laifuka a teku, yana mai cewa yanzu haka sun damke 5 daga cikinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.