Colombia
‘Yan tawayen FARC sun tabbatar da tsagaita wuta
Kungiyar ‘Yan Tawayen FARC da ke kasar Colombia ta sanar da dakatar da kai duk wani hari a fadin kasar daga ranar asabar mai zuwa. Kungiyar ta sanar da daukar matakin ne a Cuba inda ta ke tattaunawar zaman lafiya. Kuma ta jadda cewar muddin ba a kai mata hari ba ita kuwa ba za ta dauki makami ta afkawa wani ba.
Wallafawa ranar:
Talla
Amma Shugaban kasar Juan Manuel Santos ya ce shi ba zai janye sojoji daga yankin ba domin ‘yan tawayen na iya amfani da haka wajen tara makamai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu