Amurka
Obama ya ce jami'an CIA sun azabtar da jama'a
Shugaban Amurka Barack Obama, ya ce ko shakka babu, jami’an hukumar leken asirin kasar wato CIA, sun azabtar da mutane masu tarin yawa a sassa daban na duniya bayan faruwar harin ranar 9 ga watan satumbar 2001 da aka kai wa Amurka.
Wallafawa ranar:
Talla
Obama ya ce an yi hakan ne tare da amincewar majalisun dokokin kasar, duk da cewa wasu daga cikin hanyoyin da aka yi amfani da su domin tatsar bayanai daga wadanda ake zargi da aiakta ta’addanci sun kaucewa dokokin kasar ta Amurka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu