Isa ga babban shafi
Brazil-Latin

Brazil ta gudanar aikin leken asirin kasashen Latin a zamanin Soji

Wasu bayanai da aka gano, sun yi nuni da cewa tsohuwar gwamnatin kama karya ta kasar Brazil wadda ta yi mulkin kasar daga 1964-1985, ta gudanar da ayyukan leken asiri akan kasashe makwabtanta da ke yankin Latin Amurka kamar yadda wata jarida da ake bugawa a kasar mai suna Estado de Sao Pauo ta kwarmata.

Dilma Rousseff, Shugabar kasar Brazil
Dilma Rousseff, Shugabar kasar Brazil REUTERS/Ueslei Marcelino
Talla

Rahotanni sun ce jaridar ta wallafa wannan labari ne a daidai lokacin da ministan harkokin wajen kasar Antonio Patriota ke shirin yin furuci a game da wannan batu sakamakon yadda tsohon jami’in leken asirin kasar Amurka Edward Snowden ya tsegunta wannan labari ga sauran kasashen duniya.

Jaridar tace wasu takardu a Ofishin babban hafsan Sojin Brazil sun nuna an gudanar da aikin leken asirin dubarun sojin wasu kasashe ne a yankin Latin Amurka.

Kasashen da kuma aka gudanar da binciken dubarun tsarin tafiyar da aikin Sojinsu sun hada da Bolivia da Colombia da Venezuela saboda tunanin za su iya abkawa Brazil.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.