Syria
Sojan Syria 84 Sun Balle Zuwa Bangaren 'Yan Adawa
‘Yan adawa na kasar Syria dake gudun hijira a kasashen waje na ci gaba da hankoron ganin an samar da Gwamnatin rikon kwarya a kasar su.Babban Kwamishina mai kula da hakkin dan adam na Majalisar Dinkin Duniya Navi Pillay ya fito fili ya soki bangaren Gwamnatin Bashar al-Assad da kuma na ‘yan adawan saboda yadda makamai ke hannun jamaa.A halin da ake ciki Sojojin Gwamnatin Syria masu yawan gaske ne suka koma bangaren ‘yan adawa inda suka tsere zuwa kasar Turkiyya.Bayanai na cewa yawan sojan da suka balle sun kai 85.
Wallafawa ranar: