Jamus ta tabbatar da sako ma’aikatan agaji da aka yi garkuwa da su a Yemen
Ma’aikatar harakokin wajen kasar Jamus tace an sako ma’aikatan agaji hudu, da aka yi garkuwa da su a kasar Yamen, kuma tuni aka mika su hannu jami’an Majalisar Dinkin Duniya, da ke birnin Sanaa.Kasar jamus ta yi murnan sako mutanen ‘yan kasashen Colombia, Jamus, Iraqi da Faladinu, da aka yi awon gaba da su a ranar Talata, yayin da suke aikin agaji a yankin.
Wallafawa ranar:
Kabilun kasar Yamen sun shafe fiye da shekaru 15 suna garkuwa da ‘yan kasashen waje da ke kasar, don samun biyan wasu bukatunsu daga hukumomin kasar, inda daga baya su sake su, ba tare da musu ko da kwarzane ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu